Yadda ‘yan Kamaru Masu Masaukin Baƙi Suka ji da Rashin Nasara a Gasar Afcon


Wasanni

Wasu mazauna Kamaru mai masaukin baƙi a gasar Kofin Ƙasashen Afirka ta Afcon 2021 sun bayyana wa BBC Hausa halin da suka shiga bayan doke tawagar ƙasar da Masar ta yi a wasansu na yammacin Alhamis.

Bayan shafe minti 90 ana gumurzu, babu wanda ya yi nasara. Aalkalin wasa ya kara minti 30, inda a nan ma ba a samu wanda ya yi nasara ba har sai da aka je ga bugun fanareti.

A nan ne Masar ta doke Kamarun da ci 3-1.

Yanzu dai Masar za ta buga wasan ƙarshe da Senegal ranar Lahadi.

Golan Masar, Gabaski, ya yi kokari ta hanyar kaɗe ƙwallo biyu, yayin da daya ta tsallaka saman raga.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

%d bloggers like this: