Tinubu Ya Roƙi Ma’aikatan Lafiya Su Janye Yajin Aiki


Daga Wakilinmu


Shugaban ya yi wannan roƙo ne a ranar Litinin lokacin da ya gana da shugabannin ƙungiyar ta gamayyar ma’aikatan lafiya na ƙasa.


A lokacin ganawar, Tinubu ya ɗauki alƙawarin cewa zai magance matsalolin da ke addabar ɓangaren na lafiya.


Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya ke shirye-shiryen tsunduma yajin aiki a ranar Laraba mai zuwa sanadiyyar tsadar man fetur.


A makon da ya gabata ne mambobin ƙungiyar ma’aikatan lafiyar suka fara yajin aiki domin neman gwamnati ta biya musu wasu buƙatu da suka gabatar.


A lokacin da ya yi jawabi sa’ilin ziyarar tasu ga sabon shugaban ƙasa, shugaban riƙon ƙwarya na ƙungiyar, Dr Obinna Ogbonna ya buƙaci shugaban ƙasar da ya tabbatar da an zuba jari sosai a ɓangaren na lafiya a Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

%d bloggers like this: