Jakadanmu Ba Zai Fice Daga Nijar Ba – Macron


Daga Wakilinmu


Jakadan Faransa a Nijar zai ci gaba da zama a cikin kasar duk da matsin lamba daga sojojin da suka yi juyin mulki, in ji Shugaba Emmanuel Macron.


Macron a jawabinsa ga jakadun kasashen waje ya jaddada goyon bayansa ga hamɓararren shugaban Nijar, Mohamed Bazoum wanda ya ce ba zai yi murabus ba.


A cewar Macron wannan matakin ya nuna Bazoum mutum ne mai karfin hali.


Wa’adin sa’o’i 48 da aka bai wa jakadan Faransar, Sylvian Itte domin ya bar Nijar ya riga ya cika.


Macron ya kara da cewa Faransa ba za ta canza matsayinta ba na yin Allawadai da juyin mulkin soji a Nijar tare da nuna goyon bayanta ga Bazoum.


Tun a ranar 26 ga watan Yuli ne sojoji karkashin jagorancin Janar Tchiani suka kifar da gwamnatin shugaba Bazoum.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

%d bloggers like this: